For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Afenifere Ta Zargi Tinubu Da Aiwatar Da Mulkin Kama Karya

Ƙungiyar Afenifere ta zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da neman koma wa salon mulkin kama-karya irin na Janar Sani Abacha.

Ƙungiyar ta bayyana shirinta na kafa wata ƙungiyar siyasa don ƙwace mulki daga hannun gwamnati mai ci a zaben 2027.

Sakataren Yaɗa Labarai na Afenifere, Justice Faloye, ya yi wannan tsokaci ne a wata hira da aka yi da shi a wata kafar talabijin a Lagos.

Faloye ya bayyana mulkin Tinubu tun bayan hawansa kan mulki a shekarar 2023 a matsayin gazawa mai girma, inda yake cin zarafin wadanda suka saɓa masa a ra’ayi.

Ya ƙara da cewa gwamnatin na cin mutuncin shugaban ƙungiyar ƙwadago da kuma tsare mutane saboda shiga zanga-zangar ƙin jinin yunwar da gwamnatin Tinubu da jawowa ƴan Najeriya.

Faloye ya yi zargin cewa an hana ƴancin zanga-zanga a ƙarƙashin mulkin Tinubu, inda masu zanga-zanga suke fuskantar tsarewa ba bisa ƙa’ida ba.

Har ila yau, ya ce al’ummomin duniya sun yi Allah wadai da mulkin Tinubu bisa zargin kama mutanen da ke yin zanga-zanga cikin lumana a cikin tsarin dimokaraɗiyya.

Afenifere ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya saurari shawarar Farfesa Wole Soyinka kan gujewa kama-karya a Najeriya.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa, idan ba a ɗauki mataki ba, Najeriya na iya komawa zamanin kama-karya irin na mulkin soja.

A ƙarshe, Faloye ya bayyana cewa Afenifere na duba yiwuwar kafa wata jam’iyyar siyasa don tabbatar da gaskiya da adalci a Najeriya.

Comments
Loading...