For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

An Rufe Taron Kolin EU Bayan Amincewa Da Kakabawa Rasha Takunkumi Zagaye Na Tara

An rufe taron kolin Tarayyar Turai, EU, na lokacin hunturu a Brussel, babban birnin kasar Belgium a daren jiya agogon kasar.

Shugaban majalisar zartarwa na EU, Charles Michel, ya bayyana wa manema labarai a gurin taron da aka gudanar, cewa, shugabannin kasashen EU sun amince da shirin kakabawa Rasha takunkumi zagaye na tara.

Haka kuma, a cikin taron kolin a wannan rana, shugabannin kasashen EU sun amince da ba da tallafin tattalin arziki na euro biliyan 18 a hukumance ga kasar Ukraine a shekarar 2023 mai zuwa.

A daidai lokacin kuma, an amince da Bosnia da Herzegovina a matsayin ‘yan takarar neman shiga Tarayyar Turai a hukumance.

CRI Hausa

Comments
Loading...