For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

An Sanya Ranar Kammala Aikin Gyaran Wutar Yankunan Gagarawa, Hadejia Da Nguru

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya, TCN, ya fara aikin gyaran ƙarfen tawa ta 16 da ya karye a Ƙauyen Gunduwawa da ke Ƙaramar Hukumar Gezewa a Jihar Kano.

Shugaban Sashin Hulɗa da Jama’a na kamfanin, Ndidi Mbah ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da rabawa manema labarai a yau Asabar.

Ya bayyana cewa, ɗankwangilar da ke aikin gyaran ya koma bakin aikinsa a jiya Juma’a tare da bayar da tabbacin cewa, za a kammala gyaran ƙarfen tawar a ranar Alhamis 22 ga watan nan.

Idan za a iya tunawa, wata babbar motar tirela mai ɗauke da dakon kwantena ce ta bi ta kan ƙarfen tawar a ranar Lahadin da ta gabata, inda tai sanadiyar karyewarsa, abin da ya jawo rasa wuta ga al’ummu da dama da ke yankunan Gagarawa, Hadejia da kuma Nguru.

Comments
Loading...