For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Argentina Ta Bayar Da Hutun Yini Daya Don Murnar Lashe Kofin Duniya

Gwamnatin Argentina ta sanar da hutun kwana daya a kasar a jiya, don murnar lashe kofin gasar cin kofin kwallon kafa na FIFA da aka kammala ranar Lahadi a Qatar.

Rahotanni na cewa, a yau da safe ne, ake sa ran tawagar ’yan wasan Argentina za ta isa Buenos Aires, babban birnin kasar, inda shugaban kasar zai tarbe su a yau din, daga bisani kuma gwamnatin kasar za ta shirya musu wani gagarumin bikin taya murna a hukumance.

CRI Hausa

Comments
Loading...