For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Atiku Abubakar Ya Hadu Da Nyesom Wike Bayan Zaben Fidda Gwani

Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar Peoples Democratic Party, PDP, Alhaji Atiku Abubakar, a yau Litinin, ya hadu da Gwamnan Jihar Rivers, Nyesom Wike a Abuja.

Atiku dai ya kayar da Wike ne a zaben fidda gwani na masu neman takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar PDP wanda aka gudanar ranar Asabar din da ta gabata a Abuja.

Ganawar ta yau Litinin, an baiyana cewa an yi ta ne domin a sasanta bangarorin guda biyu tare da karawa PDP karfin lashe zaben shekarar 2023.

Ganawar ta samu halartar tsohon Gwamnan Jihar Ekiti kuma wanda ya nemi takarar Shugaban Kasa a PDP, Ayodele Fayose tare da sauran manyan jam’iyyar ta PDP.

Cikakken bayani kan ganawar ba ta baiyana karara ba a dai-dai lokacin rubuta wannan labarin, sai dai kuma wakilin PUNCH ya gano cewa, Atiku na kokarin neman abokin takara ne a matsayin Mataimakin Shugaban Kasa wanda zai fito da Kudancin Najeriya.

Comments
Loading...