For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Buhari Ya Kori Wata Babbar Jami’ar Gwamnatinsa Daga Aiki

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya soke nadin da aka yiwa Saratu Umar a matsayin Shugabar Hukumar Bunkasa Sanya Hannun Jari ta Najeriya, NIPC, nan take.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ne ya sanar da hakan a jawabin da ya saki a jiya Alhamis a Abuja.

A umarnin da aka baiwa Ministan Ciniki, Masana’antu da Sanya Hannun Jari, Adeniyi Adebayo, shugaban kasar ya yi umarnin cewa, darakta mafi girma a ma’aikatar ta NIPC ne zai maye gurbin Saratu a matsayin riko.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, NAN ya rawaito a baya cewa, Shugaba Buhari ya amince da sake nada Saratu Umar a watan July na 2022 domin yin wani wa’adin na shekaru biyar a matsayin shugabar ma’aikatar ta NIPC.

Saratu dai ta fara rike mukamin shugabar NIPC ne a watan Yuli na shekarar 2014.

NAN

Comments
Loading...