For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Buhari Ya Rantsar Da Sambo A Matsayin Karamin Minista

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a yau Juma’a ya rantsar da Alhaji Muazu Sambo a matsayin Karamin Ministan Aiyuka da Gidaje.

Sambo ya karbi rantsuwar ne a gaban shugaban kasa a farfajiyar Majalissar Zartarwa da ke fadar shugaban kasa a Abuja.

A yanzu haka Sambo shine wakilin jihar Taraba a Majalissar Zartarwa ta Najeriya tun baya tube Saleh Mamman da shugaba Buhari yai a kwanakin baya.

Sabon ministan wanda Injiniyan Gine-gine ne, a farkon satin nan ne Majalissar Dattawa ta tantance shi bayan ta karbi sunansa daga shugaban kasa a makon da ya gabata.

Comments
Loading...