Sign in
Sign in
Recover your password.
A password will be e-mailed to you.
Browsing Category
News
Tinubu Ya Amince Da Ajjiye Aikin Mai Magana Da Yawunsa, Yai Masa Fatan Alheri
Fadar Shugaban ƙasa ta sanar da karbar takardar ajiye aiki na dindindin daga mai Magana da Yawun Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, Ajuri Ngelale, saboda dalilai na ƙashin kansa da kuma matsalolin lafiyarsa.
Wannan ya bayyana ne a cikin wata!-->!-->!-->…
TSANANIN TSADAR FETUR: Wahala Na Jiran Iyaye, Ɗalibai Da Malamai Yayin Da Ake Shirin Komawa…
Yayin da makarantu ke shirin fara zangon karatu na 2024/2025 a faɗin Najeriya, ƙarin farashin man fetur da aka samu a makon da ya gabata ya jefa iyaye, dalibai, malamai, da masu makarantu cikin damuwa da tashin hankali.
Wasu masu!-->!-->!-->…
Zamu Fara Shirin Ɗiban Dubunnan Ƴansanda A Najeriya – Tinubu
Gwamnatin Tarayya ta yi alkawarin samar da kayan aiki na zamani ga Hukumar Ƴansandan Najeriya domin inganta ayyukanta.
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ne ya bayyana hakan a yayin bikin yaye ɗalibai 478 a Kwalejin Ƴansanda ta Najeriya da ke!-->!-->!-->…
MATATAR DANGOTE: Babu Wani Tabbas Na Samun Sauƙin Farashi – NNPCL
Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPCL) ya bayyana cewa ba shi da tabbacin cewa farashin man fetur zai ragu duk da fara ɗaukar mai daga matatar Dangote.
NNPCL zai fara ɗaukar man fetur daga matatar Dangote daga ranar 15 ga watan Satumba.!-->!-->!-->…
Dubban Faransawa Na Zanga-Zanga Kan Naɗin Sabon Firaminista
Dubban masu zanga-zanga sun fito kan tituna a sassan Ƙasar Faransa yau Asabar don yin watsi da nadin Michel Barnier a matsayin Firaminista da zargin shugaba Emmanuel Macron da karbar mulki ta ƙarfi.
Zanga-zangar ta gudana ne a birnin!-->!-->!-->…
Gwamnati Zata Na Cajar N50 A Kan Duk Hada-Hadar Kuɗin Da Ta Kai N10, 000 A OPay
Bankin Yanar Gizo na OPay ya sanar da sabon haraji na N50 akan duk wata hada-hadar da ta kai N10, 000 ko sama da haka, tsarin da aka samar bisa ga dokokin Hukumar Tara Kudaden Haraji ta Kasa (FIRS).
Daga ranar Litinin, 9 ga Satumba,!-->!-->!-->…
DA ƊUMI-ƊUMI: Mai Magana Da Yawun Shugaba Tinubu, Ngelale Ya Tafi Hutun Sai Baba Ta Gani
Mai bai wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai, Ajuri Ngelale, ya tafi hutun sai baba ta gani saboda rashin lafiya ba tare da shiri ba.
Ngelale ya bayyana cewa ya ɗauki wannan matakin ne bayan shawarwari da!-->!-->!-->…
Talauci A Najeriya Zai Zarce Hasashen Bankin Duniya Kwanan Nan Saboda Tsadar Man Fetur
Masana tattalin arziƙi sun yi gargaɗin cewa adadin ƴan Najeriya da ke ƙasa da layin talauci na iya zarce hasashen Bankin Duniya na mutane miliyan 104, sakamakon hauhawar farashin fetur da matsalolin samar da abinci da ƙasar ke fuskanta.
!-->!-->!-->…
Mun Fi Son A Rage Tsadar Kuɗin Makaranta Maimakon A Bamu Bashi – Ɗalibai Ga Gwamnati
Ƙungiyar Ɗaliban Najeriya (NANS) ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta rage tsadar kuɗin karatu maimakon samar da tsarin bashi ga ɗalibai.
Shugaban Ƙungiyar, Henry Okuomo ne ya bayyana hakan a jiya Juma’a, a wata hira da aka yi da shi a!-->!-->!-->…
BASHIN KARATU: Mun Fara Jin Alat Na Kuɗin Rijistar Ɗalibanmu – Shugaban Wata Makaranta
Shugaban makarantar Moshood Abiola Polytechnic, MAPOLY, da ke Abeokuta, Dr. Adeoye Odedeji, ya ce ɗaliban makarantar sun fara samun kuɗi na bashin karatun da suka nema.
Odedeji ya bayyana hakan ne ranar Juma’a a Abeokuta yayin rantsar!-->!-->!-->…
Ku Kare Kanku Daga Ƴanta’add, Gwamnan Katsina Ya Shawarci Ƴan Jiharsa
Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda, ya yi kira ga al’ummar jihar da su ɗauki matakan kariya don kare kansu daga hare-haren ƴanbindiga da ke addabar jihar.
Ya bayyana hakan ne a taron dandalin tattaunawa da aka gudanar mai taken:!-->!-->!-->…
Mutane 13, 346 Aka Kashe, Aka Sace 9,207 A Watanni 16 Na Mulkin Tinubu, In Ji Wani Rahoto
Tun bayan rantsar da Shugaba Bola Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu, 2023, Najeriya ta fuskanci ƙaruwar tashin hankali, inda aka kashe mutane 13,346 aka kuma yi garkuwa da 9,207 a fadin kasar.
Wannan ƙaruwar tashin hankalin da ta shafi!-->!-->!-->…
Tinubu Na Ƙoƙarin Ɗabbaƙa Cigaban Ababen More Rayuwa Irin Na China A Najeriya
Shugaban kasa Bola Tinubu ya nuna kudirinsa na kwaikwayon cigaban kasar Sin a fannin ababen more rayuwa a Najeriya bayan ziyararsa zuwa kasar.
Ya bayyana hakan ne yayin ganawa da kungiyar 'yan Najeriya mazauna kasar Sin (NIDO China) da!-->!-->!-->…
Ba Mu Hana Ƴan Ƙasa Da Shekara 18 Rubuta WASSCE Da NECO Ba – Ministan Ilimi
Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta fayyace cewa ba ta dakatar da ɗaliban da ba su kai shekara 18 ba daga rubuta jarrabawar WASSCE ko NECO.
Ƙaramin Ministan Ilimi, Dr. Yusuf Sununu ne ya bayyana haka a Abuja yayin da yake amsa tambayoyi daga!-->!-->!-->…
A Shirye Nake Na Ɗau Duk Wasu Tsauraran Matakai Don Ciyar Da Najeriya Gaba – Tinubu
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa yana shirye ya ɗauki tsauraran matakai don ciyar da ƙasa gaba, duk da cewa ba koyaushe ake samun haɗin kan ƴan ƙasa kan batutuwan ba.
Tinubu ya yi wannan bayani ne a Beijing lokacin da yake!-->!-->!-->…
NANS Ta Roƙi Gwamnati Da Ta Janye Sokewar Da Tai Wa Digirin Benin Da Togo
Shugabannin Ƙungiyar Ɗaliban Najeriya ta NANS a yankin kudu maso yamma sun roƙi gwamnatin tarayya da ta sake nazari kan soke shaidar karatun digiri daga manyan makarantu na ƙasar Benin da Togo.
A cikin wata sanarwa da Shugaban Reshen!-->!-->!-->…
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 152, Sun Kama 109, Sun Ceto Mutane 91
Sojoji sun kashe ƴan ta’adda 152, sun kama 109, sun ceto mutane 91 da aka yi garkuwa da su, a yayin da suke yaƙi da matsalar tsaro a fadin kasar nan cikin makon da ya gabata.
Sojojin sun kai hari kan sansanonin wasu manyan shugabannin!-->!-->!-->…
Yanda Ƴanbindiga Suka Ciyar Da Karnukansu Naman Direban Ƴan’uwana – Wani Malami A Sokoto
Sheikh Bashar Danfili, wani sannanen malami a Jihar Sokoto, ya nemi taimakon kudi daga jama’a bayan ƴan bindiga sun sace ƴan’uwansa guda shida a hanyarsu zuwa wani ƙauye a jihar.
Ya bayyana hakan ne a cikin wani gajeren bidiyo da ya!-->!-->!-->…
Kukah Ya Roƙi Shugabannin APC Da Su Janye Ƙarin Kuɗin Man Fetur A Kan Ƴan Najeriya
Bishop Mathew Hassan Kukah na Cocin Katolika ta Sokoto ya yi kira ga shugabannin jam’iyyar APC mai mulki da su rage farashin man fetur da ake sayarwa, yana mai cewa ƴan Najeriya na cikin halin yunwa.
Ya yi wannan jawabi ne a yau Juma'a!-->!-->!-->…
Ƴanta’adda Sun Mayar Mu Bayi, Suna Sa Mu Aiki A Gonakinsu – Ƴan Jihar Niger
Mutanen da ke zaune a wasu garuruwa da ke fama da matsalar tsaro a Ƙaramar Hukumar Shiroro da ke Jihar Neja, sun koka cewa ƴan ta’adda da ƴan bindiga na bautar da su wajen aikin gona a gonakin su.
An gano cewar, shugaban wata ƙungiyar!-->!-->!-->…