Sign in
Sign in
Recover your password.
A password will be e-mailed to you.
Browsing Category
Top News
Gamayyar Marassa Rinjaye A Majalissar Wakilai Ta Nemi A Gaggauta Janye Ƙarin Farashin Mai
Gamayyar marassa rinjaye a Majalisar Wakilai ta nemi a gaggauta janye ƙarin farashin man fetur da aka ƙara kwanan nan, saboda hakan zai ƙara wa 'yan Najeriya wahala.
Sanarwar da shugabansu Kingsley Chinda ya fitar ta ce wannan ƙarin!-->!-->!-->…
Kano Pillars Ta Sanyan Hannu Kan Ɗaukar Sababbin Ƴan Wasa 12, Ta Kuma Riƙe Ƴan Wasa 20 Gabanin Kakar…
Tawagar Kano Pillars FC, wacce ta lashe gasar Nigeria Premier Football League, NPFL, sau hudu, ta sanar da sababbin ‘yan wasan da ta dauka a hukumance gabanin kakar wasanni ta 2024/25.
An gudanar da taron bikin bayyana ‘yan wasan a!-->!-->!-->…
YANZU-YANZU: Ɗaliban Najeriya Zasu Rufe Duk Manyan Birane, Yayin Da NANS Ta Ba Da Sanarwar Fara…
Kungiyar Daliban Najeriya, NANS, ta fitar da sanarwar shirin rufe dukkan manyan biranen Najeriya, daga ranar 15 ga Satumba, 2024.
Zanga-zangar na da nufin nuna rashin amincewa da ƙarin farashin man fetur da kuma zargin rashin kwarewa da!-->!-->!-->…
Kotun Amurka Ta Ɗaure Ƴan Najeriya Kan Laifin Damfarar Dala Miliyan 5
Wata Kotun Tarayya a Amurka ta yanke wa wasu ‘yan Najeriya biyu, Franklin Okwonna da Ebuka Umeti, hukuncin zaman gidan yari bisa laifin da suka aikata na damfara ta intanet da ta yaudari mutane sama da dala miliyan $5.
Wannan bayani ya!-->!-->!-->…
Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49% Cikin Shekara Biyar A Jigawa – Hukuma
Daraktan Kiwon Lafiya a Matakin Farko na Jihar Jigawa, Dr. Shehu Sambo, ya ce adadin rigakafi ya karu daga kashi bakwai cikin dari a shekarar 2016 zuwa kashi 49 cikin dari a shekarar 2021.
Sambo ya bayyana hakan ne yau Laraba a Dutse,!-->!-->!-->…
Gwamnatin Jigawa Za Ta Kafa Cibiyoyin Kula Da Ciwon Ƙoda Biyar A Jihar
Gwamnatin Jihar Jigawa ta shirya kafa cibiyoyin kula da ciwon ƙoda guda biyar a jihar, kamar yanda Kwamishinan Lafiya, Dr. Muhammed Kainuwa ya bayyana.
Kainuwa ya bayyana hakan ne a Dutse yayin buɗe taron karɓar takardun neman kwangilar!-->!-->!-->…
Kwalara Ta Yi Ajalin Mutane 7 A Jigawa
Daga: Lukman Dahiru
An samu ɓarkewar cutar amai da gudawa a Ƙaramar Hukumar Kirikasamma ta Jihar Jigawa, wadda ta yi sanadiyyar mutuwar mutane bakwai, yayin da aka kwantar da wasu da dama a asibiti.
Shugaban kula da lafiyar al’umma!-->!-->!-->!-->!-->…
Yawan Wutar Lantarki Ya Kai Megawatt 5,313, Karo na Farko Cikin Shekaru 3 – Minista
Yawan wutar lantarki a Najeriya ya karu zuwa megawatt 5,313 a ranar Litinin da ta gabata, karo na farko cikin shekaru uku, a cewar Ma’aikatar Wutar Lantarki.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Bolaji Tunji, Mai ba da shawara ta!-->!-->!-->…
Fursunoni 3,590 Na Jiran Hukuncin Kisa A Najeriya – NCoS
Akalla fursunoni 3,590 ne da ke cikin gidajen gyaran hali a fadin Najeriya ke jiran hukuncin kisa, kamar yanda Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Najeriya (NCoS) ta bayyana.
Mai magana da yawun hukumar, Mataimakin ACC Abubakar Umar,!-->!-->!-->…
NNPCL: NLC Ta Kira Zaman Gaggawa Kan Ƙarin Farashin Fetur
Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya, NLC, ta bayyana shirinta na yin zaman gaggawa dangane da karin kashi 45 cikin 100 a farashin man fetur da Kamfanin Man Fetur na Najeriya, NNPCL, ya yi kwanan nan.
Wannan na zuwa ne yayin da ƙungiyar ta!-->!-->!-->…
Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kakkaɓe Ƴanbindiga Yayin Da Minista, CDS Suka Isa Sokoto
A jiya ne Gwamnatin Tarayya ta bakin Ƙaramin Ministan Tsaro, Dr. Bello Matawalle, ta sha alwashin kakkaɓe ƴanbindiga da sauran gungun masu aikata laifuka da ke addabar yankin arewa maso yamma, biyo bayan umarnin Shugaban Kasa Bola Tinubu!-->…
HAUHAWAR FARASHI: FCCPC Ta Janye Shirinta Na Daidaita Farashin Kayayyaki A Najeriya
Biyo bayan cece-kuce da aka samu game da barazanar da Hukumar Kula da Gasar Kasuwanci da Kare Haƙƙin Masu Sayen Kaya ta Kasa (FCCPC) ta yi na shiga tsakani kan hauhawar farashin kayayyaki, hukumar ta bayyana cewa ba za ta shiga cikin!-->…
NLC Ta Yi Watsi Da Ƙarin Kuɗin Man Fetur, Ta Ce Gwamnati Ta Saɓa Alƙawarin Da Aka Yi Da Ita
Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta ce ƙarin farashin fetur da aka yi kwanan nan abin firgici ne da tayar da hankali.
NLC ta kuma ce Gwamnatin Tarayya ta yi mata kafar ungulu bayan yarjejeniyar da suka cimma yayin tattaunawa kan mafi!-->!-->!-->…
Gwamnan Jigawa Ya Jagoranci Tawaga Zuwa Taron Ƙoli Kan Tsarin Abinci Na Afirka A Kigali
Gwamnan Jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, ya jagoranci tawagar jihar zuwa taron shekara-shekara na Tsarin Abinci na Afirka na shekarar 2024, wanda aka fara a ranar Litinin a Kigali, Rwanda.
Halartar Gwamnan taron na nuna ƙudirin Jihar!-->!-->!-->…
Jihar Kebbi Ta Raba Motocin Ɗaukar Majinyata Ga Asibitoci Don Sauƙaƙa Jigilar Marasa Lafiya
Gwamnatin Jihar Kebbi ta raba motocin ɗaukar majinyata na zamani ga asibitocin jihar don sauƙaƙa jigilar marasa lafiya zuwa manyan cibiyoyin lafiya.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Alhaji Yunusa Musa Ismail, ne ya miƙa makullin motocin ga!-->!-->!-->…
Nan Da Awa 48 Man Dangote Zai Shiga Gidajen Mai, An Kuma Bayyana Yanda Farashi Zai Kasance
Mamallakin matatar mai da ke Lagos, Aliko Dangote, a yau Talata ya yi bayani kan yanda za a saka farashin fetur da matatarsa mai tace ganga 650,000 a kowace rana zata fara sayarwa.
Dangote ya bayyana cewa da zarar kamfaninsa ya kammala!-->!-->!-->…
Kamfanin NNPC Ya Ƙara Farashin Man Fetur A Najeriya
Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPCL) ya ƙara farashin man fetur daga ₦568 zuwa ₦855, ₦897 (dangane da wurin sayarwa), duk da ƙarancin fetur da kuma halin da ƙasar ke ciki.
Rahotanni kan sabon karin farashin sun biyo bayan furucin da!-->!-->!-->…
Gurfanar Da Masu Zanga-Zangar #EndBadGovernance Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — NANS
Ƙungiyar Ɗaliban Najeriya (NANS) ta bayyana damuwarta game da gurfanar da mutanen da suka shiga zanga-zangar #EndBadGovernance.
Ƙungiyar ɗaliban ta bayyana matakin shari'a da aka ɗauka a matsayin babbar barazana ga dimokuradiyya a!-->!-->!-->…
YANZUNNAN: Zanga-Zanga Ta Barke A Abuja Kan Karancin Fetur
Wasu masu zanga-zanga sun mamaye titunan Abuja a yau Litinin suna neman a sauke Shugaban Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPCL), Mele Kyari, bisa matsalar karancin fetur da ke addabar kasar.
Zanga-zangar ta biyo bayan amincewar Kamfanin!-->!-->!-->…
PDP Na Tattaunawa Da Kwankwaso Da Peter Obi Kan Zaɓen 2027 — Kakakin Jam’iyyar
Jam’iyyar PDP ta fara tattaunawa da tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Kwankwaso da kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP) a zaben 2023, Mista Peter Obi, kan zaben 2027 mai zuwa.
Mataimakin Kakakin Jam’iyyar PDP na!-->!-->!-->…