For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Daraktan Kungiyar Gwamnonin APC Ya Ajjiye Aiki Saboda Rikicin Jam’iyya

Daraktan Janar na Kungiyar Gwamnonin Jam’iyyar APC, Salihu Mohammed Lukman, ya ajjiye aiki saboda rikice-rikicen da suka dabaibaiye jam’iyyar game da Babban Taronta na kasa.

Lukman ya ajjiye aikin ne a yau Litinin saboda rabuwar da aka samu a tsakanin gwamnonin jam’iyyar lokacin zaman da sukai a daren jiya Lahadi a Abuja.

Wasu majiyoyi da suka bukaci a boye sunayensu, sun bayyana cewa, tuni Lukman ya mika takardar ajjiye aikin nasa ga Shugaban Kungiyar Gwamnonin APC kuma Gwamnan Jihar Kebbi, Atiku Bagudu.

KU KARANTA: APC Ta Sa Ranar 25 Ga Fabarairu Domin Zaben Shugabaninta Na Kasa

Majiyar ta sanar da cewa, wasu daga cikin gwamnonin suna bukatar ajjiye aikin Lukman ko kuma ma a kore shi, abin da ya jawo ajjiye aikin nasa.

An gano cewa, duk da mafi yawa daga cikin gwamnonin suna son Lukman ya cigaba da kasancewa a kujerar, kadan daga cikinsu sun takura sai ya tafi.

Comments
Loading...