For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Faransa Na Adawa Da Shirin Turai Na Goyon Bayan Saka Hijabi

Daga: BBC Hausa

Gwamnatin Faransa ta yi Allah wadai da wani kamfen da ɓangaren kare haƙƙin ɗan Adam na majalisar Turai ta ƙaddamar a intanet da nufin ƙarfafa amincewa da tsarin sanya hijabi ga mata a Musulunci.

Matakin wanda ya samu goyon bayan ƙungiyar Tarayyar Turai kuma take ɗaukar nauyi – yanzu an janye shi.

Shirin ya ƙunshi fuskokin mata, wasu sanye da mayafi ko hijabi wasu kuma babu.

Taken shirin shi ne: “Ado yana cikin bambance-bambance kamar yadda sanya hijabi ƴanci ne; ya kamata a girmama hijabi.”

Majalisar Turai mai hedikwata a Strasbourg ta ce matakin na cikin shirinta na yaƙi da kyamar musulmi.

Amma a Faransa, ɓangarorin siyasa ne suka mayar da martani.

Ministar matasa a gwamnatin shugaba Macron, Sarah el-Hairy ta ce shirin wani matakin na ƙarfafa sanya hijabi ya saɓa wa aƙidun Faransa.

Eric Zemmour da ke neman takarar shugaban ƙasa da za a yi watan Afrilu mai zuwa, ya faɗi a Twitter cewa: “Musulunci addini ne da ya saɓawa ƴanci, kuma wannan maƙiyin gaskiya ne.”

Saboda adawa da matakin a Faransa, majalisar Turai ta janye kamfen ɗin tana mai cewa za ta bi wasu hanyoyi na isar da saƙon.

Comments
Loading...