For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Firaministan Birtaniya, Boris Johnson Ya Yi Murabus

Firaministan Birtaniya Boris Johnson ya sauka daga shugabancin jam’iyyarsa ta Conservative a jiya Alhamis.

Amma zai ci gaba da kasancewa firaministan kasar har zuwa watan Oktoba.

Za a naɗa sabon shugaban jam’iyyar Conservative a wannan bazarar sannan za a yi sabon firaminista a watan Oktoba ɗin.

Boris Johnson ya gabatar da jawabin yin murabus ɗin nasa a gaban fadar No 10 Dawning Street.

Tun kafin ya kammala yin murabus ɗin a hukumance, har an fara kamfe kan wanda zai gaje shi.

Gabanin yin bayanin murabus din a hukumance an jiyo wani mai magana da yawun fadar Gida Mai Lamba 10 ya ce: “Firaministan zai yi sanarwa ga ƴan ƙasar zuwa an ji ma.”

Mr Johnson ya yi magana ne da Sir Graham Brady, shugaban kwamitin jam’iyyar Conservative na 1922 , inda ya sanar da shi matakin da ya ɗauka, a cewar wata majiya daga fadar No 10.

Majiyar ta ƙara da cewa: “Firaminsita ya yi magana da Graham Brady inda ya amince ya sauka a kan lokaci don ba da damar naɗa wani sabon shugaban a Oktoba.”

Me Boris Johnson Ya Ce A Jawabinsa?

Firaministan ya ce a yanzu ta bayyana cewa burin majalisar dokokin shi ne a samu sabon shugaban Jam’iyyar Conservative kafin a naɗa sabon firaminista.

Johnson ya ce a yanzu za a fara bin tsarin sabon shugaba kuma za a sanar da jadawalin hakan a mako mai zuwa.

“Na amince da abin da Sir Graham Brady ya ce, kan cewa yanzu za a fara shirin zabar sabon shugaba kuma za a sanar da jadawalin a mako mai zuwa.”

Johnson ya ci gaba da cewa ya fi ƙarfin a sauya shi a siyasa.

Tsarinmu mai kyau na zabar shugaba zai samar da wani sabon shugaban.

(BBC HAUSA)

Comments
Loading...