For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Gwamna Badaru Ya Yi Tituna da Dakunan Karatu a Kwalejin Gumel – Dr. Galadi

Daga: Saifuddin Madaci

Mukaddashin shugaban makarantar horas da malaman makaranta dake Gumel a jihar Jigawa, Dr. Dauda Abu Galadi, ya yabawa gwamnatin jihar bisa aiwatar musu da aiyukan cigaba a makarantar.

Da yake bayyana irin aiyukan da gwamnatin ta yi mu su yace, an shinfida musu hanyoyi a cikin makarantar masu tsawon kilomita 10, wanda  ya bayyana hakan a matsayin abinda zai magance musu matsalolin da ke ci musu tuwo a kwarya.

Gwamnatin Muhammadu Badaru Abubakar ce ta yi musu wannan aikin, tare da gina wasu a jujuwa 4 na daukar darasi masu daukar dalibai 250, da dakunan kwanan dalibai maza da mata da gyaran ofishoshin wasu malamai, da kuma gina gadajen kananan malamai dana mayan malamai a makarantar da dai sauransu.

Haka kuma ya ce irin tunanin da mai girma gwamna ya dasa akwakwalen al’ummar jihar, na karasa aiki da wani ya fara a jihar, inda ya bayyana shi a matsayin mutum jajirtatce kuma mai zurfin tunani.

Kazalika Dr. Dauda ya bayyana bukatar dake akwai na basu damar daukar wasu malamai domin koyar da daliban ingantatcen ilimi mai nagarta.

Comments
Loading...