For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Gwamnatin Kano Zata Ginawa Malaman Makaranta Da Sauran Ma’aikata Gidaje 5000

Majalissar Jihar Kano ta amince da kudirin samar da gidaje 5000 domin malaman makaranta, ma’aikatan gwamnati da kuma sauran ma’aikata a jihar.

Da yake karanta takardar kudirin, Kakakin Majalissar Jihar Kano, Hamisu Ibrahim Chidari ya ce, Majalissar Zartarwar Jihar Kano tana bukatar a amince mata domin ta samar da gidajen a dukkanin kananan hukumomin jihar guda 44.

Bayan yin dogon nazari, ‘yan majalissar sun amince da kudirin samar da gidajen karkashin kulawar Shugaban Hukumar Kula da Aiwatar da Tsare-tsare da Aiyuka, Rabi’u Sulaiman Bichi.

Comments
Loading...