For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Kotu Ta Hana Jam’iyyar PDP Rushe Shugabancin Jihar Kano Dake Yiwa Kwankwaso Biyayya

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin dakatar da shugabancin jam’iyyar PDP na ƙasa daga rushe shugabannin jam’iyyar na Jihar Kano.

Alƙali Taiwo O. Taiwo a hukuncin da ya yi, ya gargaɗi PDP da cewar, ta bar shugabancinta na Jihar Kano daga matakin mazaɓu zuwa jiha su ci gaba da gudana har zuwa lokacin da za a yanke hukunci a kan ƙarar da aka shigar.

Jam’iyyar PDP a Jihar Kano na cikin tsaka mai wuya, musamman ganin shirye-shiryen fitar tsohon gwamnan jihar, Rabi’u Musa Kwankwaso daga jam’iyyar zuwa NNPP.

Kwankwaso dai shine jagoran jam’iyyar a jihar kuma ana ganin cewa shugabancin jam’iyyar na ƙarƙashinsa, abin da ya sa wasu ke neman da a rushe shi.

A kwanakin baya, TASKAR YANCI ta rawaito cewa wasu jiga-jigai a cikin tafiyar Kwankwasiya sun je wajen tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, inda suka baiyana cewa su ba zasu bi Kwankwaso zuwa NNPP ba, sannan suka buƙaci da a rushe shugabancin jam’iyyar na jihar wanda ke yiwa Kwankwaso biyayya.

Comments
Loading...