For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Kotun Ƙararrakin Zaɓe Ta Soke Nasarar Wani Ɗan Majalissa

Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓen Ƴan Majalissun Tarayya da ke zamanta a Asaba ta Jihar Delta, ta soke nasarar da Ɗan Majalissar Wakilai mai wakiltar mazaɓar Aniocha/Oshimili, Mr. Ngozi Okolie ya samu a zaɓen ranar 25 ga watan Fabarairu.

Okolie wanda ɗan jam’iyyar Labour Party ne, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa ta bayyana shi a matsayin wanda yai nasara a wancan zaɓe.

Ku Karanta: Mafi Yawan Shugabannin Najeriya Suna Da Ƙarancin Sanin Mene Ne Ci Gaba – Obasanjo

To sai dai kuma tsohon Shugaban Marassa Rinjaye na Majalissar Wakilai, kuma ɗan takarar jam’iyyar PDP a wannan zaɓe, Ndidi Elumelu ya ƙalubalanci nasarar a gaban kotun, yana buƙatar a soke nasarar ta Okolie.

A ƙarar da Elumelu ya shigar mai lamba EPT/DL/HR/06/2023, ya ce, ba jam’iyyar Labour Party ba ce ta ɗau nauyin takarar Okolie, sannan kuma bai ajjiye aikinsa na gwamnati ba a lokacin takarar.

A hukuncinta, kotun mai alƙalai 3, wadda Alkali A.Z. Mussa ke jagoranta, ta soke nasarar Okolie bisa rashin cancanta inda ta ce wanda ya biyo bayansa a yawan ƙuri’u wato Elumelu ne yai nasara.

Kotun ta ce, Okolie bai samu ɗaukar nauyin jam’iyyar Labour Party ba yanda yake a doka, saboda shi ba ɗan jam’iyyar ba ne a daidai ranar 28 ga watan Mayu, 2022 lokacin da aka gudanar da zaɓen fidda gwani a jam’iyyar.

Kotun ta kuma ce, wanda ake ƙarar wato Okolie, bai ajjiye aikin gwamnatinsa ba domin ya tsaya takarar.

Comments
Loading...