Ƙungiyar kwallon kafar mata ta Najeriya ta doke takwararta ta Amurka a bugun fenariti da ci 4-3 domin zuwa zagayen kusa da na ƙarshe bayan tashi 1-1 a gasar cin kofin ɗuniya ta mata ‘yan kasa da shekara 17 da ake gudnarwa a Indiya.
Edafe Omamuzo ce ta ci kwallon karshe da ya bai wa matan na Najeriya nasara a birnin Mumbai.
An dai samu jinkiri sa’a ɓiyu kafin soma buga wasan sakamakon sawa na ruwan sama da aka samu, inda Omamuzo ta fara cin kwallo a minti na 26.
Sai dai takwararta ta Amurka Amalia ta farke musu bayan da kwallon da ta buga ya dagi ‘yar wasan Najeriya kafin shiga raga..
Ɓayan tashi 1-1, sai aka je zuwa bugun fenariti, inda Najeriya ta sami nasara bayan doƙe takwarorinsu mata na Amurka.
Daga: BBC Hausa