For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Magoya Bayan Morocco Na Sa Ran Matsayi Na Uku A World Cup

Magoya bayan Moroko sun shirya tsaf domin nuna farin ciki da wasan neman na uku da kasarsu za ta yi da Croatia a wasa na biyun karshe a gasar cin kofin duniya.

Moroko ce kasar Afrika ta farko kuma ta Larabawa da ta fara zuwa wasan kusa da na karshe a duniya, amma ta yi rashin sa’a a wasan a hannun Faransa mai rike da kofin.

Birnin Casablanca ya yi tsit tun bayan rashin nasarar da kasar ta yi a hannun Faransa a ranar Laraba.

Magoya bayan sun ce ba su ji dadain sakamakon wasan ba, amma suna jin cewa suna alfahari da kasarsu.

Mutane da dama dai suna tsammanin ba za a ga magoya bayan ba da yawa, saboda rashin da nasarar da ta yi a baya.

BBC Hausa

Comments
Loading...