For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

NDLEA Ta Kara Wa’adin Daukar Sabbin Ma’aikatan Da Take Yi

Shugaban Hukumar Hana Sha da Fatucin Miyagun Kwayoyi, NDLEA, Buba Marwa, ya amince da kara wa’adin sati guda kafin a rufe shafin daukar sabbin ma’aikata na hukumar.

Buba Marwa ya bayyana hakan ne a sanarwar da Daraktan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a na hukumar, Femi Babafemi ya fitar a jiya Alhamis a Abuja.

Sanarwar ta bayyana cewa, an yi karin ne domin bayar da dama ga masu neman aikin wadanda suka sami tasgaro a kokarinsu na cike neman aikin.

An dai bude shafin daukar sabbin ma’aikatan ne a ranar Lahadi, 12 ga watan Maris, inda aka tsara rufe shi a gobe Asabar, 8 ga watan Afirilu, 2023.

To amma yanzu da karin sati gudan da NDLEA ta yi, za a rufe shafin daukar ma’aikatan ne da misalin karfe 11:59 na daren ranar 17 ga watan Afirilu, 2023.

NAN

Comments
Loading...