Allah Ya yi wa Sarkin Gaya a jihar Kano Alhaji Ibrahim Abdulkadir rasuwa a yau Laraba.
Mai bai wa Shugaba Muhammadu Buhari shawara kan kafofin sada zumunta Bashir Ahmad ne ya wallafa hakan a shafinsa na Facebook.
Acewar sanarwar da sakataren gwamnatin jihar ya fitar nan gaba kadan za ta fitar da sanarwar a hukumance.
Sarki Ibrahim Abdulkadir ya rasu ne bayan ya sha fama da rashin lafiyar da ba a bayyana ba.
Sarkin ya rasu yana da shekara 91, kuma ya shafe shekaru 30 yana mulkin Gaya wanda a daga baya ya zama Sarki a shekarar 2020.
Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ne ya mayar da Sarkin Gaya Sarki mai daraja ta daya, tare da sauran masaratu uku a jihar Kano.