For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Tinubu Ya Naɗa Madadin Garba Shehu Da Wasu Muƙaman Da Dama

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa tshohon Babban Manaja kuma Editan Jaridar Leadership, Kingsley Stanley Nkwocha, a matsayin Babban Mai Temakawa Shugaban Ƙasa, SSA a ɓangaren Kafafen Yaɗa Labarai da Sadarwa.

Shugaban ya naɗa Nkwocha ne tare da wasu da za su yi aiki a ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa.

Waɗanda Tinubun ya naɗa domin yin aiki a ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasar sun haɗa da Tope Fasua a matsayin Mai Bayar da Shawara kan Harkokin Tattalin Arziƙi a Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa.

KARANTA WANNAN: Tinubu Ya Naɗa Jamila Da Ayodele A Matsayin Ministocin Matasa

Sauran naɗe-naɗen na ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasar sun haɗa da Sadiq S Jambo a matsayin Mai Bayar da Shawara kan Tattalin Arziƙi; Dr. Muhammad Bulama a matsayin Babban Mai Temakawa kan Aiyuka na Musamman; Mahmud Muhammad, Mai Temakawa na Musamman kan Harkokin Gida a Arewa Maso Gabas; da kuma Ahmed Ningi a matsayin Babban Mai Temakawa kan Kafafen Sadarwa na Zamani da Kai wa Ɗaukin Gaggawa.

Haka kuma Shugaban Ƙasar ya naɗa marubuci a jaridu kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Gimba Kakanda a matsayin Babban Mai Temakawa kan Harkokin Bincike da Bayar da Bayanai a ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa.

Comments
Loading...