For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Tunisia Ta Fitar Da Najeriya Daga Gasar Cin Kofin Afirka

Tunisia ta fitar da Najeriya daga gasar cin kofin Afirka a Kamaru, inda ta samu sa’ar Super Eagles da ci 1 – 0.

Tunisia yanzu za ta hadu da Burkina Faso a kwata fainal.

Najeriya ta buga kusan rabin wasan ne da mutum 10 bayan Alex Iwobi ya karbi jan kati.

Dan wasan Youssef Msakni ne ya ci wa Tunisia kwallonta a raga, minti biyu da dawowa hutun rabin lokaci.

Sakamakon ya bada mamaki ganin yadda Najeriya ita ce kasar da ta ci dukkanin wasanninta uku a zagayen farko, kuma wadda korona ba ta yi wa illa ba.

Tunisia wacce ta lashe kofin a 2004, a ranar Asabar za ta hadu da Burkina Faso, 29 ga watan Janairu.

(BBC Hausa)

Comments
Loading...