For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Wani Mutum Ya Yi Karar Pastor Saboda Ya Kwace Masa Mata

Wani mutum mai suna Mr. Joel Udoh ya yi karar Ifeanyi na Cocin Loves Chapel a gaban kotun Majistare ta 39 a Kano saboda zarginsa da kwace masa mata.

Lauyan mai karar, Yusuf Ali Faragai ya ce, mai karar ya yi karar malaminsa na cocin Lovers Chapel da ke yankin Sabongari a Kano saboda zarginsa da kwace masa mata ta hanyar jan hankalinta.

Lokacin da aka gabatar da maganar a kotun, wanda ake zargin ya musanta aikata laifin.

Mr. Joel daya ne daga cikin mabiya cocin Pastor Ifeanyi da ke unguwar Sabongari a Kano.

A bangarensa, Alkalin Kotun Majistare, Mustapha Hassan ya bayar da umarnin bincikar lamarin ga ‘yansandan da ke Zone One a Kano.

(NIGERIAN TRACKER)

Comments
Loading...