For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Wasu Makiyaya Sun Kashe Mutane 11, Sun Ƙone Gidaje A Benue

Mutanen da ba su gaza 11 ba ne aka tabbatar sun mutu a ƙauyukan Igama da Edumoga Ehaje da ke Ƙaramar Hukumar Okpokwu ta Jihar Benue.

Ana zargin makiyaya da kai harin wanda ya faru a jiya Lahadi.

An sanar da jaridar THE NATION cewa, maharan sun kuma ƙone gidaje da dama a garuruwan.

Harin dai ya sanya fargaba a zukatan makwabtan ƙauyuka, waɗanda aka ce sun ƙauracewa gidajensu, bayan faruwar lamarin a jiya.

Sanata Abba Moro ya tabbatar da faruwar lamarin kan ƙauyukan biyu a wani rubutu da yai a dandalin Facebook.

Sanatan dai shi ma ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Okpokwu ne, inda ƙauyukan da aka kai wa harin suke.

Mai magana da yawun ƴansanda a Jihar Benue, Kate Anene ba ta daga kiran da akai mata ba, haka kuma, ba ta amsa sakon kar-ta-kwanan da wakilin THE NATION ya tura mata ba.

Comments
Loading...