Majalisar Zartarwar Kasa ta amince da karawa jami’an ‘yansanda albashi da kaso 20 cikin 100.
Ministan Ma’aikatar ‘Yansanda, Maigari Dingyadi, ya bayyana hakan ne a yau, bayan kammala zaman majalisar zartarwar wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta, a fadarsa dake Abuja.
KU KARANTA:
- ‘Yansanda Sun Kama Sojan-Gona Na Cutar Masu A Daidaita Sahu A Kano
- Neman Aikin Kwastom Na Shekarar 2021 Ga Masu Diploma Da NCE
- An Samu Korafe-Korafen Fyade Guda 11,200 A Najeriya Cikin Shekarar 2020
Ministan ya ce ana sa ran sabon karin albashin zai fara aiki daga watan Janairu na shekarar 2022.
Kazalika, Majalisar Zartarwar ta amince da kashe Naira Biliyan 13.100 domin biyan hakkokin ‘yan sanda dubu 5,472 wanda suka mutu a lokacin da suke bakin aiki daga shekarar 2013 zuwa 2020.