For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

YANZU-YANZU: Har Yanzu Dai, Buhari Ya Nemi Majalissa Ta Yi Gyaran Dokar Zabe

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya rubuta wa Majalissar Dattawa bukatar sake gyara sabuwar dokar zaben da ya sanya wa hannu a Juma’ar da ta gabata.

A wasikar da Shugaban Kasar ya rubuta wadda Shugaban Majalissar Dattawa Ahmad Lawan ya karanta a zaman Majalissar na yau, Shugaban ya bukaci Majalissar da ta duba yiwuwar goge sashi na 84(12) na Dokar Zabe ta 2022.

Sashin dai shine wanda yake magana a kan ajjiye aikin masu rike da mukaman siyasa kafin su shiga sabgar zaben fidda gwani.

Shugaban Kasar ya baiyana sashin a matsayin mai nuna wariya ga masu rike da mukaman siyasa.

Comments
Loading...