For real, reliable, and timely news updates on national and global events.

Ƙungiyar Yarabawa Ta Matsa Kan Samar Da Ƴansandan Jihohi Da Gudanar Da Cikakkiyar Fedaraliya

Ƙungiyar Yarabawa ta Afenifere ta koka kan yawaitar matsalar tsaro a wasu sassa na ƙasar nan saboda hare-haren wasu makiyaya masu ɗauke da makamai kan manoma.

Ƙungiyar ta bayyana cewar, munanan aiyukan laifin da ƴanbindigar ke aikatawa a kan manoma ya jawo ƙarin buƙatar samar da ƴansandan jihohi domin inganta tsaro tun daga tushe.

Wannan kira na ƙungiyar na ɗauke ne a cikin sanarwar bayan taro da Babban Sakataren Ƙungiyar, Chief Sola Ebiseni ya rabawa manema labarai a jiya Laraba a Ogbo Ijebu ta Jihar Ogun.

Ƙungiyar ta ƙara jaddada adawarta da yin kiwo a buɗe kamar yanda aka saba, sannan kuma ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta yi amfani da rahoton Taron Ƙasa na 2014 ko kuma rahoton Kwamitin Nasir El-Rufai kan samar da cikakken tsarin fedaraliya domin gyara kudin tsarin mulkin Najeriya na 1999.

Comments
Loading...